Majalisar Dattawa ta janye dakatarwar da ta yi wa Sanata Abdul Ningi, kuma ta umarceshi ya bayyana a gabanta

0
22

Majalisar Dattawan Najeriya ta yafe wa Sanata Abdul Ahmed Ningi tare da janye dakatarwar da ta yi masa tun daga ranar 12 ga watan Maris.

 

Majalisar ta ɗauki matakin ne bayan Sanata Abba Moro ya gabatar da ƙudirin neman afuwarta a madadinsa kuma “ya ɗauki alhakin dukkan” abin da ya faru a zaman da suka yi yau Talata.

 

Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya siffanta Ningi a matsayin “mai hazaƙa” kuma ya ce sun ɗauki matakin ne “ba tare da nuna ɓangaranci ba”.

Dakatarwar da aka yi wa sanatan mai wakiltar Mazaɓar Bauchi ta Tsakiya ta tsawon wata ta jawo cecekuce a majalisar da ma faɗin ƙasar a watan Maris.

 

Ƙudirin da majalisar ta zartar a lokacin ya zargi Abdul Ningi da “zubar da ƙimar majalisa” bayan ya zargi shugabanninta da sake yin wani kasafin kuɗi na 2024 bayan wanda ‘yan majalisar suka amince da shi a bainar jama’a.

 

Majalisar dattijai ta yi afuwa tare da kiran Sanata Abdul Ahmed Ningi da aka dakatar a ranar 12 ga watan Maris, 2024, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito.

 

An bayyana Neman shi ne bayan wani kudiri da mataimakin shugaban marasa rinjaye Sanata Abba Moro ya gabatar, wanda ya nuna nadama a madadin Sanatan da aka dakatar.

Sanata Abba Moro ya yi alkawarin daukar cikakken alhakin abin da Ningi ya aikata, tare da amincewa da tsananin dakatarwar.

 

Halin da Sanatan ya yi a lokacin dakatarwar ya kasance abin dubawa da muhawara a cikin majalisar.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya jaddada basirar sanatan tare da bayyana shi a matsayin dan majalisar dattijai mai kima, inda ya kara da cewa matakin kiran Sanata Ningi ya wuce rarrabuwar kawuna na addini da kabilanci.

 

 

 

Hafsat Ibrahim