Ministan yada labarai da al’adu Mr Lai Muhammed yace shirya fina-finai na iya kawo dorewar hadin kan Najeriya.

0
118

An yi kira ga masu shirya fina-finan Najeriya dasu yi amfani da basirarsu wajen shirya fina-finai don dorewar hadin kan Najeriya da kuma bunkasa al’adun Afirka ga kasashen waje.

 Ministan yada labarai da al’adu na Najeriya Alhaji Lai Muhammed ya yi wannan kiran a lokacin da yake ba da kyaututtuka a bikin rufe bikin fina-finai na Zuma da aka gudanar a Abuja, Najeriya.

 Daga kalaman sa,Ministan ya ce, bikin fina-finai na wannan shekara ya nuna wa masu shirya fina-finai yadda za su yi amfani da sababbin dandamali ba kawai don ganin kudaden ba, amma  don karuwar riba da kuma isa ga fina-finai na duniya.”

 Ministan ya yi nuni da cewa, yana alfahari da cewa, masana’antar fina-finan Najeriya a yau ta zama muhimmin dandali na baje kolin fasaha da al’adun kasar ga kasashen waje.

 A nata jawabin, Karamar Ministar Babban Birnin Tarayya, , Dakta Ramatu Aliyu, ta ce, dole ne a baiwa Nollywood goyon bayan da ya dace domin samun ci gaba da kuma yin takara mai inganci a kasuwar fina-finai ta duniya.

 Dakta Aliyu ta yi kira ga ’ya’yan masana’antun Najeriya da su hada kai su tabbatar da gasa mai inganci a tsakaninsu.

 Shima da yake nasa jawabin, Manajan Darakta na Kamfanin Fina-Finai na Najeriya Mista Chidia Maduekwe ya yi imanin cewa, tattalin arzikin Najeriya na iya kara bunkasa ne kawai idan an tallafa wa shirye-shirye kamar bikin fina-finan na Zuma.

 Ya kara da cewa fina-finan Najeriya ya karu matuka saboda yadda ake iya samar da ayyukan yi da wadata tare da samar da zaman lafiya da hadin kan kasa.

 Mista Maduekwe ya yabawa gwamnati wajen ci gaba da jajircewa wajen inganta ci gaban fannin ta hanyar aiwatar da manyan tsare-tsare na manufofin da aka samu.

 Koli na bikin fina-finai na Zuma, ya bayar da kyautuka ga wadanda suka yi nasara na rayuwa da kuma fitattun jarumai da furodusosi.

 Fitaccen jarumin fina-finan shine Ikechukwu Ike daga Najeriya, mafi kyawun hoto shine Uche Udo daga Najeriya, fitaccen fim din kasar waje ya tafi Bangladesh, yayin da fitaccen jarumin fina-finan ya tafi Kanzi Zange daga Jamhuriyar Jama’ar China.

  1. Daga Fatima Abubakar.