Rundunar sojin saman Najeriya Ba Ta Daukan Ma’aikata – Kakakin

0
20

 

Rundunar sojin saman Najeriya ta yi watsi da wani tallan daukar ma’aikata da ake yadawa a shafukan sada zumunta a matsayin na bogi da yunkurin damfarar masu neman aiki.

Sanarwar da Daraktan Hulda da Jama’a da Yada Labarai na NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya fitar ranar Litinin a Abuja ta ce “NAF ba ta daukar ma’aikata”, ya kuma gargadi masu neman kar su fada hannun ‘yan damfara.

Gabkwet ya ce wannan tallar ba ta fito daga hukumar NAF ba, kuma ya tunatar da ‘yan Najeriya cewa kwanan nan hukumar ta yaye ma’aikatan da suka fara daukar ma’aikata na Basic Soja Course 43/2022, a ranar 8 ga watan Yuli.

A cewarsa, za a sanar da jama’a isassun bayanai a duk lokacin da NAF ke daukar ma’aikata.

“Ana kara tunatar da jama’a cewa daukar ma’aikata da tsarin sa a NAF kyauta ne. Duk wanda ya biya kudi a karkashin ko wane irin salo yana yin haka ne bisa kasadar sa.

Bugu da kari tsarin daukar ma’aikata NAF ba shi da ma’aikatan daukar ma’aikata, don haka duk wanda ya ce yana gudanar da wannan aiki a madadin NAF dan damfara ne.

Hukumar ta NAF tana so ta shawarci masu neman aikin da su gaggauta kai rahoton duk wanda ya nemi a biya shi ga sashin NAF mafi kusa ko kuma rundunar ‘yan sandan Najeriya,” inji shi.

 Firdausi Musa Dantsoho