An kaddamar da gyare-gyaren tituna 135, na gundumomi da dama a Abuja.

0
30

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Mista Nyesom Wike, ya gargadi ‘yan kwangilar da ke kula da aikin gyaran hanyoyi 135 a babban birnin tarayya da ma’aikatun farar hula a kan bambancin kwangila.

Wike, wanda ya yi wannan gargadin a yayin kaddamar da ayyukan a Abuja ranar Litinin, ya bayyana cewa za a kammala ayyukan nan da watanni shida.

A cewarsa, babban birnin tarayya Abuja za ta biya duk ‘yan kwangilar kudadensu domin su samu damar kammala aikin cikin wa’adin da aka amince mu su.

“Ga ‘yan kwangila, bari in gargade ku yanzu, duk waɗannan abubuwan da kuke yi da ayyukan injiniya ba za mu amince da shi ba.

“Muna da kudin da za mu biya ku. Don haka ku yi abinda ya dace.

Ya kuma gargadi babban sakatare na hukumar babban birnin tarayya, Mista Olusade Adesola da kada ya kawo wata takarda da ke neman a sake nazari ko kuma wani fayil kan batutuwan da ba a yi tsammani ba, yana mai cewa “an yi la’akari da komai”.

Ministan ya bukaci mazauna yankin da su tallafa wa ‘yan kwangilar domin su samu damar kammala aikin a kan lokaci, ya kara da cewa babu wani ci gaba da ke zuwa ba tare da radadi ba.

Ya kuma nemi goyon bayan sarakunan gargajiya domin tabbatar da cewa matasa da duk mazauna yankunansu sun tallafa wa ‘yan kwangilar domin su kai aikin a kan lokaci.

Hakazalika Wike ya godewa shugaban karamar hukumar Abuja, Mista Christopher Maikalangu, da ya bayyana a bainar jama’a ,shugabannin kansilolin yankin sun yanke shawarar yin aiki da hukumar babban birnin tarayya Abuja domin amfanin mazauna babban birnin tarayya Abuja.

Tun da farko, karamar ministar babban birnin tarayya, Dakta Mariya Mahmoud, ta bayyana cewa, hukumar babban birnin tarayya Abuja ta samu gagarumar nasara wajen kawo sauyi a babban birnin kasar, makonni uku kacal da fara aikin Mista Project (Wike).

MMriya ta ce an magance matsalar hasken titi; ana fama da matsalar tsaftar mahalli, kuma yanzu za a canza ababen more rayuwa a hanyoyin da za su yi tasiri ga mazauna.

Har ila yau, babban sakatare na FCTA, Adesola, ya bayyana cewa ayyukan sun hada  da gyaran tituna 135 da ake da su da kuma gyaran gadoji a gundumomi daban-daban na babban birnin tarayya Abuja.

“Wannan aiki na kawo sauyi a cewarsa, zai yi matukar tasiri ga rayuwar al’ummar babban birnin tarayya,” inji shi.

Ya bukaci ‘yan kwangilar da su cika wa’adin da aka amince da su na gudanar da ayyukan, yana mai cewa “kudin ku na nan za  a biya; ya rage nnau kyyi aiki kuma a biya ku.

A nasa bangaren, Mista Ahmed Hadi, Sakataren zartarwa na Hukumar Raya Babban Birnin Tarayya, ya yi nuni da cewa, dimbin hanyoyin da aka bunkasa tun shekarar 1980 sun tabarbare.

Hadi ya ce aikin zai hada da tarwatsawa tare da cire kwalta da ake da su a wasu wurare yayin da a wasu wuraren kuma za a yi aikin rufe kwalta.

Ya ce za a gudanar da hanyoyi 135 a Wuse, Garki, wasu unguwannin Maitama da Asokoro, wanda zai kai tsawon kilomita 42.

“Idan aka kammala, za a inganta zirga-zirgar ababen hawa da rage lokacin tafiye-tafiye kuma hanyoyin za su kasance mafi aminci,” in ji shi.

Shugaban kwamitin majalisar kan FCT, Mista Muktar Betara, ya nuna kwarin gwiwa ga ikon Wike na samar da ajandar kawo sauyi ga FCT.

Ya kuma tabbatar wa da ministan na goyon bayan kwamitin don ba shi damar samun nasara a aikinsa na mayar da FCT matsayin wurin da duk ‘yan Najeriya ke so.

Hakazalika, Ona na Abaji, Alhaji Adamu Yunusa, ya godewa ministan bisa daukar wani katafaren mataki na isar da ribar dimokuradiyya ga mazauna birnin tare da ba shi tabbacin goyon bayan majalisar gargajiya.

A nasa jawabin, Maikalangu ya yabawa Wike bisa wannan gagarumin abin yabawa, sannan ya yi kira da a kara kaimi ga al’ummar karkara domin kara kaimi ga kokarin kananan hukumomin shida na bunkasa ci gaba a yankin.

Ya kuma baiwa ministan tabbacin goyon bayan shugabannin majalisar domin ganin an kammala ayyukan.

Da yake mayar da martani a madadin ‘yan kwangilar, Mista Obada Zabadne, babban jami’in gudanarwa na ZBMC Ltd, ya amince da kwarin gwiwa da amincewar gwamnati na samar da ayyuka masu inganci.

Ya kuma tabbatar wa da ministan cewa ‘yan kwangilar sun jajirce wajen cimma abin da ya wuce yadda ake tsammani da kuma cikin lokacin da aka amince.

 

Daga Fatima Abubakar.