An kafa dokar hana zirga-zirga a jihar Adamawa yayin da wasu dauke da makamai suka kutsa cikin rumbunnan ma’aikatar agajin gaggawa ta NEMA.

0
44

“An bayar da rahoton cewa ‘yan bindigar sun kai hari kan mutane da adduna tare da kutsawa cikin harabar kasuwanci, suna kwashe dukiyoyi.”

“Tsarin dokar za ta takaita zirga-zirga a duk fadin jihar, kuma wadanda ke kan muhimman ayyuka da ke da ingantacciyar shaida ne kawai za a ba su izinin tafiya yayin lokacin dokar.”

Gwamnan ya yi kira ga ‘yan kasa da mazauna jihar da su bi wannan umarni, inda ya jaddada cewa duk wanda aka samu ya saba wa dokar za a kama shi kuma ya fuskanci fushin doka.

Fintiri ya tabbatar wa al’ummar Adamawa kudurinsa na tabbatar da tsaro da tsaro, inda ya bukace su da su kwantar da hankalinsu da bin doka da oda.

Wannan ci gaban ya zo ne makonni biyu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani kantin sayar da kayayyaki a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.

‘Yan barandan da ke da yawan gaske sun kai farmaki gidan ajiyar da ke kusa da Birged 6 na Sojoji inda suka yi awon gaba da buhunan masara da shinkafa da aka sarrafa a gida da dai sauran kayayyaki na miliyoyin Naira.

Gidan ajiyar na wani dan majalisar jiha ne kuma tsohon shugaban karamar hukumar Sardauna.

Daya daga cikin masu gadin gidan ajiyar da ya bukaci a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya cewa a lokacin da matasan suka fara haduwa da misalin karfe 11:50 na dare, an sanar da sojoji da ‘yan sanda.

Ya ce kafin isowar jami’an tsaro tuni matasan suka kutsa cikin rumbun ajiyar.

Jami’in tsaron ya kara da cewa da isar su jami’an tsaron sun yi harbin kan mai uwa da wabi don tarwatsa ‘yan fashin kuma ana cikin haka an harbe biyu.

An kai harin ne a dakin ajiyar kaya a lokacin tarzomar EndSARS na shekarar 2020 kuma an yi awon gaba da kayayyaki na miliyoyin naira.

 

Daga Fatima Abubakar.