Hukumar Babban Birnin Tarayya ta kafa kwamitin mutane 6 don warware rikicin NULGE a kananan hukumomi.

0
13

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike ya shiga cikin rikicin da ya barke tsakanin shugabannin kananan hukumomin shidda da kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Najeriya ta shirya yajin aikin.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da NUGLE ta tsayar da ranar 2 ga watan Oktoba, domin fara yajin aikin hadin guiwa da kungiyar malamai ta Najeriya (NUT) da suka shiga yajin aikin tun bayan dawo da makarantu a yankin na shekarar 2023/2024.

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Talata bayan wata ‘yar gajeriyar ganawar sirri da shugabannin kananan hukumomi shida da jami’an NUGLE, ministan ya bayyana cewa an kafa kwamitin da zai warware matsalolin cikin makonni biyu.

Wike ya ce nan da sa’o’i 48 masu zuwa ya kamata a magance dukkan matsalolin da ke tada jijiyoyin wuya a tsakanin jam’iyyun.

“Mun kafa wani kwamiti da zai fito da hanyoyin da za a magance matsalar.

“Mun yi imanin cewa NUGLE ta gamsu da shirye-shiryen da aka yi a kasa don magance wadannan matsalolin.

“Na yi imanin cewa nan da sa’o’i 48 masu zuwa ya kamata NUGLE ta yi abin da ake bukata saboda bukatun jama’a.”

Da yake gabatar da tambayoyi daga manema labarai bayan kammala taron, sakatariyar ma’aikatar kula da kananan hukumomi ta FCT, Bitrus Garki, ya ce batutuwan sun dame kusan kashi 40% na alawus alawus, da sauran ragi da kungiyar ke bayarwa.

Garki ya ce tun a shekarar 2006 al’amuran sun taso ne amma ministan babban birnin tarayya na yanzu ya damu da yadda za a magance su da sauran kalubalen da kananan hukumomin ke fuskanta.

“Ministan ya kafa kwamitin mutum 6 wanda ya kunshi dukkan bangarorin da abin ya shafa, daga tattaunawar da muka yi da kungiyar ta NUGLE, kungiyar ta yaba wa ministan bisa gaggawar da ya yi ta hanyar mayar da martani ga wasikar.

“Mun amince cewa da a janye yajin aikin  kafin rahoton kwamitin, daga ranar 10 ga wata mai zuwa.” Inji shi.

 

Daga Fatima Abubakar.