Jerin Kasashen Afirka 4 da suka kai wasan daf da na kusa da karshe a gasar cin kofin duniya.

0
75

Bayan shekaru 92 da yunkurin 49, wata tawagar Afirka ta kai wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya.
Morocco ta zama tawaga ta farko a Afirka da ta taba zuwa wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya bayan da ta yi nasara a kan Portugal ranar Asabar.
Kasashen Afirka sun fara fafatawa a gasar cin kofin duniya tun shekara ta 1934- Masar ta fice a shekarar 1930 sakamakon guguwa – kuma sun buga wasanni 49 a gasar.

Ayau zamu leko muku zuwa ga nazari ne kan tarihin da nahiyar Afirka ke da shi a gasar cin kofin duniya da kuma yadda kowace kungiyar ta kasance.
Gasar cin kofin duniya ta Fifa ita ce babbar gasa ta ƙwallon ƙafa na ƙasashen Afirka.

Kafin Morrocco, kasashen Afirka mafi girma sun kai ga gasar cin kofin duniya a matakin karshe na Quarter – kuma kasashe uku ne kawai suka kai matakin.
Ga Jerin kasashen Afrika da suka kai wasan daf da na kusa da karshe a gasar cin kofin duniya.
Tawagogin Afirka uku sun yi waje a matakin daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya kuma duk sun yi hakan cikin yanayi mai zafi.

1. Kasar kamaru 1990: Kamaru ta kasance kasa ta farko a Afirka da ta kai matakin takwas na karshe a Italiya a shekarar 1990.
Sun baiwa zakarun Argentina mamaki a wasan farko na gasar a San Siro kuma hakan ya sa suka ci gaba da kasancewa a rukunin da ke dauke da Romania da Tarayyar Soviet.
Daga nan ne suka doke Colombia da ci 2-1 a karin lokaci a zagaye na 16, inda Milla mai shekaru 38 ya zura kwallaye biyu a ragar Kudancin Amurka. Tare da barin nahiyar a cikin farin ciki, kungiyar ta buga wasa da Ingila a wasan kusa da na karshe.
David Platt ne ya ci wa Ingila kwallo a farkon wasan, kafin Emmanuel Kunde ya rama kwallon a minti na 61 da fara wasa. Bayan Minti hudu Eugene Ekeke ne ya baiwa Kamaru tazarar maki minti 25 kai wasan daf da na karshe a Afirka.

Sai dai Gary Lineker ya rama kwallon a bugun fenariti sannan ya ci a karin lokaci da bugun fanareti.
Kasan yammacin Afirka in sun kai matakin daf da karshe a gasar cin kofin duniya a shekarar 1990 a Italiya.

Ingila ce ta fitar da Kamaru a karin lokaci da ta samu.

2. Kasar senegal 2002:

Wata Kungiya ta yammacin Afrika ta yi kokarin kai nahiyar Afirka wasan karshe na Quarter Final a gasar cin kofin duniya ta 2002. Senegal ta bi sawun Kamaru a 2002 a Koriya ta Kudu da Japan – ta hanyoyi fiye da ɗaya. Sun doke masu rike da kofin gasar (Faransa) a wasan farko na gasar a kan hanyarsu ta neman tikitin shiga gasar.

Sun buga da Sweden a zagaye na 16 kuma, kamar yadda aka yi da Kamaru, wasan ya tafi har izuwa karin lokaci. Henri Camara ne ya zura kwallon zinare a minti na 104 da fara wasa, hakan ya kai ‘yan wasan yammacin Afirkan zuwa wasan kusa da na karshe.

A cikin takwas na ƙarshe, Turkiyya ta cire kasar ta senegal daga wasan.

3. Kasar Ghana 2010:
Black Stars ita ce kasa ta uku a Afirka da ta tsallake zuwa matakin daf da na karshe a gasar cin kofin duniya ta Fifa.

Kungiyar kwallon kafan ta Afirka ta Yamma ta taka rawar gani a tarihin gasar cin kofin duniya.
Ghana a shekara ta 2010 ta kai kusa da wasan kusa da na karshe fiye da wadanda suka gabace ta. Tawagar Afirka daya tilo da ta tsallake rukunin a waccan shekarar, kuma kamar yadda ta yi da Kamaru da Senegal wasansu na zagaye na 16 ya tafi da karin lokaci – inda Asamoah Gyan ya zura kwallo a ragar Amurka.
A wasan daf da na kusa da na karshe da Uruguay, inda aka tashi kunnen doki 1-1 a minti na 120, da gangan Luis Suarez ya ki sakin kwallon don hana Ghana ci. An kore shi daga wasan amma Gyan, bisa matsin lamba da ba zai iya jurewa ba, ya buge ragan.
Wanda hakan ya bada daman fenariti bugun daga kai sai mai tsaron gida.
A gasar Afrika ta Kudu 2010 Ghana ta sha kashi a hannun Uruguay da ci 4-4 a bugun fenariti
‘Yan Kudancin Amurka sun yi nasara a bugun daga kai sai mai tsaron gida, hakan yasa Ghana ta yi waje a wasan.

4. Kasar Moroko 2022:
Morocco ta zama kasa ta farko a Afirka da ta kai wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya a ranar Asabar bayan ta samu nasara a kan Portugal. Sun kasance kan gaba a rukuninsu a Qatar (a kan Croatia, Belgium da Canada) sannan suka doke tsoffin zakarun duniya Spain a bugun fenariti a zagaye na 16.

Maroko sau daya kawai aka zura mata kwallo a gasar cin kofin duniya.

A yau Laraba ne ‘yan arewacin Afirka za su kara da Faransa kuma za su marawa kansu baya don yin gaba a yanzu bayan tsira da manyan masu dauke da kambu da yawa.
A duk kokarin da Afrika ta yi, daga karshe Maroko ta samu nasara.

Rawar da Morocco ke takawa na nufin wani baban nasara ga yan Afirka ne gabanin gasar cin kofin duniya a nan gaba.

Fifa ba ta fayyace ba amma mai kula da wasanni ya ce Afirka zata iya dace da samun gurbi a gasar cin kofin duniya ta 2026 ta Fifa saboda rawar da Morocco ta taka.

Daga: Firdausi Musa Dantsoho