Mutane 29 Sun Mutu A Hadarin Mota A Kaduna, da Fashewar iskar gas a Kano

0
120

Mutane 29 ne suka mutu a ranar Talata a wasu manyanalamura masu tashin hankali guda biyu a jihohin Kaduna da Kano.

Lamarin na farko ya yi sanadin mutuwar fasinjoji 20 da suka mutu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a lokacin da motar bas da suke ciki ta yi karo da tirelar siminti na BUA da misalin karfe 5 na safe.

A Kano, an fitar da akalla gawarwaki tara daga karkashin baraguzan ginin da ya ruguje a unguwar Sabongari sakamakon fashewar iskar gas.Ginin yana dab da makarantar Winners Private School dake kan titin Aba. Wasu daliban makarantar sun samu raunuka a hatsarin.

Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kaduna, Hafiz Muhammad, wanda ya tabbatar da faruwar hatsarin, ya ce sun yi zargin gajiyar da direban ne saboda sun fito daga tafiya dare.

Ya ce, “Bas din ya yi karo da wata tirela ta siminti ta BUA sannan ta kama da wuta. Mutane 22 ne ke cikin motar bas din daga cikinsu manya maza 17, mata 2 da kuma karamar yarinya.

“Sun ce tirelar tana fakin ne a lokacin da motar bas ta shiga karkashinta. Abun yayi muni. Kullum muna gargadin direbobin bas gamda tafiye-tafiyen dare,” inji shi.

Ko da yake ya yarda cewa babu wata doka da ta hana tafiye-tafiye da daddare, shugaban hukumar FRSC ya ce, “Abin da ke tattare da hadari ne domin galibin hadurran da aka samu a wannan hanyar na faruwa ne saboda tafiye-tafiyen dare.”

A Kano, an yi tashin hankali a Sabongari yayin da fashewar iskar gas ta girgiza yankin da kewaye har zuwa kafuwarsu.

Sabongari yanki ne na mazauni da kasuwanci a karamar hukumar Fagge, wanda ya fi yawan jama’a da ba ‘yan asalin jihar ba.

Wani dan agajin da ya taimaka wajen kwashe wadanda suka makale a ginin ya ce ya kirga gawarwaki tara amma ‘yan sanda da gwamnatin jihar sun ce adadin wadanda suka mutu ya kai hudu da biyar.

Akwai kuma wani sirri game da musabbabin fashewar.Yayin da ‘yan sanda suka dora alhakin fashewar wani bututun iskar gas a wani shagon walda da ke gaban makarantar, mazauna yankin sun ce harin kunar bakin wake ne.

Wani mazaunin garin ya ce dan kunar bakin waken ya

so shiga makarantar mai zaman kansa ne amma aka hana shi shiga sannan ya tarwatsa kansa, inda ya kashe wasu uku.

Sai dai kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Samaila Shu’aibu Dikko da Daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) a jihar Alhassan Mohammed, sun shaida wa Aminiya cewa rahoton farko ya nuna cewa fashewar ta fito ne daga shagon walda kuma ba ta kowace hanya fashewar bam bane.

Gwamnatin jihar ta kuma tabbatar da wannan matsayin ta wata sanarwa da kwamishinan yada labarai,Muhammad Garba ya fitar, wanda ya bayyana mai walda Vincent Ezekwe daga jihar Enugu.

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, wanda ya je Kano domin ganawa da wakilan jam’iyyar APC mai mulki a kan kudirinsa na shugaban kasa, tare da gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, ya ziyarci wurin da fashewar ta afku a jiya.

Mataimakin shugaban kasan ,wanda wani mazaunin yankin da kwamishinan ‘yan sandan suka yi wa bayanin, ya ce “Mun zo nan ne domin mu gano abin da ya faru da kuma jajantawa mazauna yankin da iyalan da suka rasa ‘yan uwansu da wadanda suka jikkata. An bayyana mana cewa, fashewar wani abu ne daga shagon wani mai walda kuma da mai walda da wasu da dama, kusan tara sun rasa rayukansu sakamakon wannan lamari. Wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne matuka. Muna addu’ar Allah Ta’ala yajikan wadanda suka rasu.”

 

Ganduje ya ce jihar za ta dauki matakin daidaita sana’ar walda a wuraren da jama’a ke da yawa domin kaucewa afkuwar lamarin nan

gaba.

Fasto Mike Ajibola wanda cocinsa ke da tazarar mitoci ya ce an ceto sama da dalibai 50 da wasu ‘yan tsiraru da suka samu raunuka.

Daga:  Firdausi Musa Dantsoho