Sarkin Zazzau Ahmad Bamali,yayi kira ga mata da su jajirce wurin neman kowane ilmi idan sun samu dama.

0
88

Sarkin Zazzau, Ahmad Bamali, ya ce Najeriya na bukatar shugabannin da za su gyara matasa domin su kasance masu rikon amana a kasar nan gaba.

Sarkin ya bayyana haka ne a wajen wani taron mata da gidauniyar Women Models and Mentors Foundation ta shirya.

Ya ce, “Abin da ya rage mana a yau shi ne nasiha. Ba dole ba ne ka zama farfesa don jagorantar mutane.

“Ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don tasirin ilimin ga waɗanda ke bayanmu, musamman waɗanda ke buƙatar wasu horo na musamman da fasaha.

“Bamali ya ce,kasuwanci yana da mahimmanci. Ina sha’awar shi, musamman ma a wannan lokacin da al’amarin ya shafi mata.

“Ni daya ne daga cikin mutane da Allah Ya albarkace su da  ‘ya’ya mata. Ina da ‘yan mata hudu da namiji, don haka zan iya cewa ni uban ‘yan mata ne.

“Muna jan hankalin ‘yan mata su shiga harkar kasuwanci, musamman wadanda suka kammala makarantun Islamiyya. Mu kullum muna ce musu su hada ilimi guda biyu; ilimin yammaci da na Musulunci.

“Ba batun samun digiri ba ne. Digiri takarda ce kawai, tare da ilimin da kuka samu. Ta yaya kuka yi amfani da abin da kuka karanta?Shine abin nuni.

“Ba batun samun digiri da yawa ba ne, me kuka yi? Me za ku iya yi da hannuwanku? Abin da ya fi muhimmanci ke nan a yau, kada ku yi abubuwan da ba za su taimake ku ba a gidajen ku da kuma rayuwar ku.

A jawabinta na maraba shugabar hukumar ta WMM Bilkisu Ibrahim ta ce mata suna fuskantar matsaloli fiye da maza a fannin zamantakewa, siyasa da tattalin arziki.

“Wannan rashin daidaituwa ya bayyana ta hanyar hana mata dama ta kowane fanni na rayuwa.

“Muhimmancin samun muryoyin mata a matsayin jagoranci na zamantakewa da tattalin arziki da siyasa ba za a iya yin la’akari da shi ba saboda su ne mafi yawan jama’a.”

 

Daga Fatima Abubakar