Aisha Buhari na neman isassun jari domin rigakafin cututtukan zuciya.

0
26

Uwargidan shugaban kasa Aisha Buhari ta yi kira da a samar da isassun kudade a fannin magani da rigakafin cututtukan zuciya a kasar nan.

Aisha ta yi wannan kiran ne a ranar Larabar da ta gabata a lokacin da ta karbi wadanda suka ci gajiyar aikin tiyatar zuciya na kyauta a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin sun kasance a fadar Villa a ziyarar godiyar da suka kai wa uwargidan shugaban kasar kan taimakon da ta yi.

Uwargidan shugaban kasar ta kuma bayyana burinta na ci gaba da hada kai da sauran abokanan ci gaba a fannin kiwon lafiya wajen samar da kulawar da ta dace ga yaran iyalai marasa galihu a Najeriya.

“Ta hanyar gidauniyata Aisha Buhari da kuma Future Assured, an yi tunanin yin hadin gwiwa da sauran likitocin zuciya na duniya daga Italiya don gudanar da aikin tiyatar zuciya kyauta ga ‘yan Najeriya masu bukatar irin wadannan ayyuka.

“Tsarin ya kasance ne don ba da jinya ga mabukata, musamman yaran da ke fama da matsananciyar ciwon zuciya kuma a yau mun sami damar yin murna tare da wadanda suka ci gajiyar tiyatar da aka yi.

Don haka ta bayyana aniyar tallafawa duk wani kokari na inganta lafiyar yara marasa galihu.

“Ra’ayoyin da sabuntawa masu gamsarwa game da yadda waɗannan hanyoyin suka canza rayuwar marasa lafiya kuma danginsu koyaushe za su zama tushen abin ƙarfafa ni in yi ƙarin.

“Bisa abubuwan da aka samu a lokacin aikin zuciya, akwai babban gibi a fannin aikin tiyatar zuciya a Najeriya wanda ke bukatar jari mai yawa daga bangaren gwamnati da masu zaman kansu,” in ji ta.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, masu jawabai sun godewa jarumtakar da uwargidan shugaban kasar ta yi wajen bayar da tallafi ga marasa galihu.

Babban daraktan kula da lafiya na cibiyar kula da lafiya ta tarayya Jabi, Farfesa Sa’ad Ahmed ya nuna jin dadinsa ga uwargidan shugaban kasar bisa hadin gwiwa da likitocin kasar Italiya inda aka raba gwaninta a yayin aikin.

A cewar Ahmed, wadanda suka ci gajiyar shirin zai yi wahala su fuskanci yanayin ba tare da sa hannun uwargidan shugaban kasa ba.

Mista Murtala Dodo wanda ya ci gajiyar tallafin, ya nuna jin dadinsa ga uwargidan shugaban kasar kan yadda ta farfado da rayuwarsa bayan ya dade yana fama da cutar.

An  ruwaito cewa, a ranar 24 ga watan Janairu, uwargidan shugaban kasar ta gayyaci tawagar likitocin masu aikin tiyatar zuciya daga kasar Italiya domin yin aikin tiyatar zuciya kyauta ga yara marasa galihu a Najeriya.

 

Daga Fatima Abubakar.