An dakatar da aikin gine-gine a Gaduwa da aka gina ba bisa ka’ida ba.

0
25

An dakatar da aikin gine-gine  a ranar Talata ta yau  qn umurci wani mai wani gida a yankin Gaduwa da ya dakatar da aiki a wurin saboda kutsawa.

Daraktan sashen kula da ci gaban babban birnin tarayya Abuja, Murktar Galadima, wanda ya jagoranci sauran manyan jami’an sashen a kan wannan atisayen, ya ce ma’aikacin bai bi tsarin da aka amince da shi ba tun da farko, kuma ya mika aikin zuwa yankin lambu.

Ya ce duk da umarnin dakatar da aiki da aka yi wa gine-ginen da aka kafa ba bisa ka’ida ba, mai ginin ya gaza bin wasu sanarwar da aka ba shi.

Galadima ya bayyana cewa gwamnati ba za ta bari masu ci gaba su yi watsi da babban tsarin Abuja da sunan ci gaba a birnin ba.

Daraktan ya kuma umurci wani maginin titin Oladipo Diya, wanda har yanzu a yankin Gaduwa ya daina aiki kan wani ci gaban da ba a amince da shi.

A nasa bangaren, manajan Project na wurin, Engr Chidi Godwin, ya yi zargin cewa akwai amincewar da jami’an FCTA suka ba su.

Daga Fatima Abubakar