Gwamnatin tarayya ta bayyana ainihin dalilin tsadar abinci

0
35

Gwamnatin tarayya ta dora alhakin tsadar kayan abinci a Najeriya kan hauhawar farashin kayayyaki da fasa kwauri.

 POLITICS NIGERIA ta ruwaito cewa, Mohammad Abubakar, ministan noma, shine ya bayyana hakan a Abuja, yayin da yake jawabi a Abuja, a karo na biyar na cin nasarar zaben shugaban kasa Muhammadu Buhari (PMB) na shekarar 2015-2023.

 Ya ce kalubalen bai takaita ga Najeriya kadai ba saboda annobar COVID-19 ta lalata tattalin arzikin kasa.

 “Kasancewar wasu nau’o’in abinci da Najeriya ke shigo da su ba ya nuna cewa muna da karancin abinci.

 “Yawan tsadar abinci da muke fuskanta a kasar nan ya samo asali ne sakamakon hauhawar farashin kayayyaki, wanda ba irin na Najeriya ba ne, amma saboda annobar COVID-19 da ta tilasta rufe wasu sassa na tattalin arziki na tsawon watanni da dama,” in ji shi. yace. 

 Ministan ya kara da cewa ana kokarin dakile safarar ‘yan ta’adda

 ‘Yan Najeriya da dama sun nuna damuwarsu kan tsadar kayan abinci da iskar gas a halin yanzu, inda suka bukaci gwamnati ta kara daukar matakan shawo kan lamarin.

 

 ‘Yan kasar dai sun ce lamarin ya sa rayuwan ta tsananta wa mutane .

Daga: Firdausi Musa Dantsoho