Ganduje ya Gayyaci Kwankwaso, Gwamna Abba da Shekarau zuwa Jam’iyyar APC

0
14

Ganduje ya Gayyaci Kwankwaso, Gwamna Abba da Shekarau zuwa Jam’iyyar AP

 

A karshe shugaban jam’iyyar APC mai mulki ta kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya gayyaci tsohon ubangidansa kuma dan takarar shugaban kasa zuwa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) domin dawo da martabar jam’iyya mai mulki.

Gwamna Ganduje ya mika irin wannan zumunci ga Gwamna Abba Kabir Yusuf da tsohon Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau zuwa APC.

Ganduje wanda ya yi wannan roko a ranar Alhamis din da ta gabata a karshen taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Kano ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki a shirye take ta dawo da daukacin ‘ya’yan jam’iyyar adawa APC.

Idan za’a iya tunawa Jaridar Tozali ta rawaito wannan taron an yi shi ne domin cika Umarnin shugaban kasa Bola Tinubu na kokarin sulhunta Kwankwaso da Ganduje domin su yi tafiya daya cikin jam’iyyar APC.

 

Hafsat Ibrahim