Shehu Abdullahi dan kwallo ya auri yar kannywood Naja’atu

0
447

Ayiri ri ! A makon daya gabata ne aka daura auren wancan shahararren dan wasan kwallo Nigeria watau Abdullahi Shehu tare da amaryarsa wacce jarumar ‘yar wasan hausa ce watau kannywood Naja’atu Muhammad Sulaiman wanda aka fi saninta da murjanatu ‘yar baba. Ta samu wannanm sunan ne a wani shaharren film da tayi mai sunan Murjanatu.

An daura auren ne ranar Jumma’an da ta gabata a garin kano

Naja’atu tafara fitowa a fina finan kannywood ne tun tana ‘yar kankanuwa kuma tayi fina finai da dama kamar suhakkin rai , auren gaja ,harira da dai sauransu. Allah ya basu zaman lafiya da zuria’a dayyiba.

Daga Maryamah Idris