DA DUMINSA: Kotu ta sauke Adeleke a matsayin gwamnan jihar Osun

0
30

 

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Osun da ke zamanta a Osogbo ta sauke gwamna Ademola Adeleke a matsayin zababben gwamnan jihar.

Kotun ta bayyana cewa ya kamata hukumar zabe ta kasa INEC ta janye takardar shaidar cin zabe da ta baiwa Adeleke na jam’iyyar Peoples Democratic Party  PDP sannan ta ba tsohon gwamna Adegboyega Oyetola na jam’iyyar APC.

Alkalin kotun, mai shari’a Tertse Kume ya karanta mafi rinjayen hukuncin, ya ce Oyetola ya samu kuri’u 314,931 da suka hada da Adeleke ya samu kuri’u 219,666.

Ana ci gaba da shari’ar ‘yan tsiraru.

A Najeriya za a tuna cewa INEC ta bayyana Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna da aka gudanar ranar 16 ga Yuli, 2022.

Daga:Firdausi Musa Dantsoho